in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
ECOWAS ta yi Allah wadai da hari a Burkina Faso wanda ya hallaka sojojin kasar
2016-12-18 12:37:06 cri
Kungiyar tarayyar tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS), ta yi Allah wadai da harin ta'addanci da aka kaddamar a sansanin sojin kasar Burkina Faso, lamarin da ya hallaka sojojin kasar 12 a ranar Juma'ar da ta gabata.

Cikin wata sanarwa da ya fitar shugaban kungiyar ta ECOWAS, ya bukaci kasashen duniya dasu dauki matakan dakile hare haren da masu ikirarin yin jihadi suke kaddamarwa.

Sojojin 12 sun gamu da ajalinsu ne, bayan da maharan su kusan 40 dauke da muggan makamai suka afkawa sansanin sojojin dake Nassoumbou, a kusa da kan iyakar kasar da Mali.

Sakamakon harin, shugaban kasar ta Burkina Faso Roch Marc Christian Kabore, ya soke ziyarar aiki da ya shirya kaiwa Najeriya, wanda da farko ya so halartar taron shugabannin kasashe mambobin ECOWAS karo na 50.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China