in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An dakile yunkurin juyin mulki a kasar Burkina Faso
2016-10-22 13:42:12 cri
Ministan tsaron kasar Burkina Faso Simon Compaore ya bayyana a jiya Jumma'a cewa, gwamnati da sojojin kasar sun dakile wani yunkurin juyin mulkin soja wanda rundunar tsaron tsohon shugaban kasar Blaise Compaore ta shirya.

A gun taron manema labarai da aka kira a wannan rana, Simon Compaore ya ce, kimanin dakarun tsohon shugaban kasar 30 ne suka kai hari a fadar shugaban kasar mai ci, da kuma sansanin soja dake birnin Ouagadougou, babban birnin kasar.

Ban da wannan kuma, sun yi yunkurin kubutar da tsohon ministan harkokin wajen kasar Janar Gilbert Diendere, da kuma kwamandan tsohuwar rundunar tsaron shugaban kasar Djibril Bassole, da ake tsare da su a wani gidan yari na soja, a wani yunkuri na kifar da shugaba mai ci a yanzu Christian Kabore .

A cewar 'yan sandan, an gano wasu mutanen da ake zarginsu da hannu a wannan lamari a ranar 8 ga wannan wata a kan hanyarsu ta zuwa Ouagadougou, kuma an harbe biyu daga cikinsu har lahira, sannan wani dan sanda guda ya ji rauni.

Ministan tsaron kasar Burkina Fason ya ce, yanzu haka an kama wasu sojoji 19 da ake zarginsu da hannu a yunkurin juyin mulkin sojan da bai samu nasara ba. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China