in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An dage bikin rantsar da shugaban kasar Zambiya
2016-08-21 12:59:44 cri
Gwamnatin kasar Zambiya ta dakatar da bikin rantsar da shugaban kasar Edgar Lungu, wanda aka sake zaba bayan da babbar jam'iyyar adawar kasar ta kalubalanci sake zaben nasa.

An bayyana shugaba Lungu, a matsayin wanda ya sake yin nasarar lashe zaben shugaban kasar a ranar 11 ga wannan wata da muke ciki, sai dai Hakainde Hichilema wanda ya yi wa babbar jam'iyyar adawar kasar UPND takara, ya kalubalanci sakamakon zaben a gaban kotu.

Sakataren gwamnatin kasar Ronald Msiska ya sanar da dakatar da shirye shiryen bikin rantsar da shugaban kasar, wanda ake shirin gudanarwa a babban dandalin taron na kasar, sai dai jam'iyyar adawar ta kalubalanci zaben a ranar Juma'ar da ta gabata.

Da farko an shirya rantsar da Mista Lungu ne a Talata mai zuwa.

Kafafen yada labarun kasar sun rawaito cewar, an ga ma'aikata na kwashe kayayyakin aikin bikin rantsuwar bayan samun umarni na dakatar da bikin.

A bisa kundin tsarin mulkin kasar, ba'a rantsar da shugaban kasa matukar an kalubalanci sakamakon zaben kasar. (Ahamd Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China