in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in Zimbabwe ya yi musu kan cewa shugaban kasar ya bukaci a kama 'yan wasan da suka shiga gasar Olympics
2016-08-27 13:38:24 cri
Wani jami'in gwamnatin kasar Zimbabwe ya bayyana a ran 26 ga wata cewa, akwai wasu kafofin watsa labarai da suka bada labarin cewa, wai shugaban kasar Robert Gabriel Mugabe ya ba da umurnin kama 'yan wasan kasar da suka shiga gasar wasannin Olympics da aka yi a birnin Rio na kasar Brazil, wannan labari ba ya da tushen gaskiya, kuma, shugaban kasar bai taba ba da irin wannan umurni ba.

Ministan kula da harkokin labarai na kasar Zimbabwe ya ce, wannan shi ne labarin karya, kuma labari ne da babu tushen gaskiya cikin sa.

Ya bayyana haka ne a yayin dake halartar wani bikin ba da kyautar kudin karatu da wani kamfanin kasar Sin ya samar wa daliban Zimbabwe.

Kaza lika, ya ce, ba ko wane dan wasa ya iya cimma lambar yabo cikin gasar wasannin Olympics ba, amma muna alfahari da dukkan 'yan wasan kasar da suka shiga gasar Olympics, duk da ko wane irin sakamako suka samu a gasar da aka yi.

Wasu kafofin watsa labaran Nijeriya sun ce, shugaban kasar Zimbabwe ya ba da umurni kama 'yan wasan kasar da suka shiga gasar wasannin Olympics a filin jirgin saman kasar, sabo da ba su samu lambobin yabo a yayin gasar Olympic da aka yi a birnin Rio na kasar Brazil. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China