in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Rasha za su sanya ido don ganin an aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a kasar Syria
2016-09-13 10:34:37 cri
Shugaban babbar hukumar gudanar da ayyuka ta hedkwatar manyan hafsan hafsoshin sojan kasar Rasha Sergei Rutskoy ya bayyana a jiya Litinin cewa, Rasha ta shirya sosai don ganin shirin tsagaita bude wuta a dukkan kasar Syria ya kai ga nasara, tare da sa ido kan bangarori daban daban na kasar don ganin sun aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a fadin kasar Syria.

Rahotannin da shafin internet na ma'aikatar tsaron kasar Rasha ya fitar, sun nuna cewa, Rutskoy ya bayyana cewa, Rasha ta fahimci cewa, yana da wuya a samun nasarar tsagaita bude wuta a kasar Syria, don haka, kasar Rasha tana fatan kasar Amurka za ta sauke nauyin da ke kanta, kana ta yin hadin gwiwa da cibiyar daidaita rikice-rikice da sulhuntawa ta kasar Rasha dake kasar Syria.

Hakazalika kuma, Rutskoy ya ce, tuni cibiyar daidaita rikice-rikice da sulhuntawa ta kasar Rasha dake kasar Syria ta tura rukunin aiki don tabbatar da ganin an tsagaita bude wuta a kasar Syria. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China