in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakadan Turkiya a Isra'ila ya mika takardar kama aiki ga shugaban kasar Isra'ila
2016-12-13 10:40:29 cri
Sabon jakadan kasar Turkiya a Isra'ila Mekin Mustafa Kemal Okem, ya mika takardar kama aiki ga shugaba Reuven Rivlin a jiya Litinin 12 ga wata, matakin dake nuna cewa, ya fara wa'adin aikin sa a matsayin jakadan Turkiya a Isra'ila. Wannan ne dai karo da farko da kasar Turkiya ta tura jakada zuwa kasar Isra'ila a cikin shekaru 6 da suka gabata.

An yi bikin mika takardar kama aikin sabon jakadan a fadar shugaban kasar Isra'ila.

Da yake jawabi yayin bikin, Mr. Okem ya bayyana cewa, hakan sabon mafari ne na raya dangantakar dake tsakanin Turkiya da Isra'ila.

Shi kuwa a nasa bangare, shugaba Rivlin cewa ya yi, wannan muhimmin lokaci ne a tarihi, yana kuma fatan kasashen biyu za su ci gaba da hadin gwiwa a fannonin tattalin arziki da cinikayya da dai sauransu. Kaza lika Mr. Rivlin ya jajantawa jama'ar Turkiya bisa harin ta'addanci da ya auku a birnin Istanbul a ranar 10 ga wata.

Kafin hakan, jakadan kasar Isra'ila dake kasar Turkiya ya riga ya isa kasar Turkiya, tuni kuma ya fara gudanar da aikinsa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China