in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi Allah wadai da harin ta'addanci a birnin Alkahira
2016-12-12 10:21:30 cri
Babban magatakardar MDD Ban Ki-moon, ya yi tir da harin ta'addancin da aka kaddamar kan wata coci dake birnin Alkahiran kasar Masar a jiya Lahadi, lamarin da ya sabbaba kisan a kalla mutane 25, tare da jikkata wasu masu ibada su 49.

Cikin wata sanarwa da kakakin sa ya fitar a jiya Lahadi, Ban Ki Moon ya yi fatan za a kai ga hukunta wadanda suka aikata wannan mummunan laifi.

Shi ma dai kwamitin tsaron MDDr ya yi kakkausan suka game da aukuwar wannan hari, yana mai cewa ya zama wajibi a hukunta wadanda suka aikata shi.

Rahotanni na cewa wasu ne da ba a tantance da su ba, suka dasa Bam din mai nauyin kilogiram 12 a majami'ar dake makare da masu ibada, wadda ke unguwar Abassiya, wanda kuma fashewarsa ta hallaka tare da jikkata mutane da dama.

Kawo yanzu dai babu wata kungiya da ta dauki alhakin kaddamar da harin, sai dai wasu na danganta shi da kungiyar ABM mai sansani a lardin Sinai dake arewacin kasar ta Masar. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China