in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban jami'i: Najeriya ta amince da tsarin kasar Sin daya tak
2016-12-11 12:46:37 cri
Wani babban jami'i a Najeriya ya bayyana a jiya Asabar cewa, kasar ta amince da tsarin kasar Sin daya tak, kuma ba za ta laminci kafa ofisoshin jakadanci biyu daga kasar Sin ba.

Jami'in ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi a taron shekara shekara na kungiyar sada zumunta tsakanin Najeriya da Sin karo na 24 a birnin Legas, ya ce a kwanan nan ne suka samu wasu labarai da ake yadawa ta shafukan internet cewa wai akwai wani sabon jakada da ake kira jakadan Taiwan har yana da ofis a Abuja.

"Sam sam ba zai yiwu ba Taiwan ta mallaki ofishin jakadanci Abuja. Sai dai za ta iya kafa ofishin kasuwanci ne kadai a Najeriya", in ji Bola Akinterinwa, kuma tsohon darakta janar a cibiyar nazarin dangantakar kasa da kasa ta Najeriya.

Shi ma tsohon jakadan Najerya a kasar Sin Jonathan Coker, ya ce ya saba ka'ida Taiwan ta nada jakada a Najeriya, ko kuma ta ce za ta kafa ofishin jakadanci.

Sola Onadipe, shi ma tsohon jakadan Najeriya a kasar Sin, ya ce dole ne Najeriya ta yi bincike game da zargin nada jakadan Taiwan a kasar. (Ahamd Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China