in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A Najeriya ana zaben 'yan majalisu a jahar Rivers mai arzikin mai
2016-12-11 12:22:43 cri
A jiya Asabar aka gudanar da zaben kujerun majalisun dattijai 3 da na wakilai 10, da kuma na majalisun dokokin jahar Rivers mai arzikin mai, duk da halin zaman dar dar da ake fuskanta a jahar.

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar INEC, ta shirya gudanar da zaben ne bayan wani hukuncin kotun tarayyaar kasar a ranar 19 ga watan Maris inda ta soke zaben majalisun dokokin wanda aka gudanar tun a shekarar 2015.

Sai dai ana fuskantar rikice rikice a lokacin zaben, lamarin da ya tilasta hukumar zaben dakatar da zaben ana tsaka da gudanar da shi.

Wakilin kamfanin dillancin labarai na Xinhua dake jahar ya rawaito cewa, an fara zaben ne a kananan hukumomi 8 a jahar, kuma an fara tantance masu kada kuri'a tun da misalin karfe 8:30 na safe. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China