in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'an tsaro a jahar Niger dake tsakiyar Najeria na cikin shirin ko ta kwana don dakile barazanar harin ta'addanci
2016-12-11 12:18:41 cri
Jami'an tsaro a jahar Niger dake tsakiyar Najeriya na zaune cikin shirin ko ta kwana domin dakile duk wata barazanar hare-haren ta'addanci da kuma tabbatar da ganin an gudanar da bukukuwan Kirsimeti na wannan shekara lami lafiya.

Moshood Jimoh, shi ne kwamandan bataliya ta 31 ta sojojin kasar, ya shedawa manema labarai a Minna babban birnin jahar Niger bayan kammala wani taron tattaunawa game da sha'anin tsaro.

Ya ce tuni hukumomin tsaron suka tanadi matakan tabbatar da tsaro gabanin gudanar da bukuwawan Kirsimeti da lokacin bukukuwan da ma bayan kammala bukukuwan.

A cewar Jimoh tuni aka girke jami'an tsaro a wasu wuraren da ake da fargaba domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China