in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta tura abinci ga 'yan gudun hijirarta dake Kamaru
2016-12-05 10:12:40 cri
Gwamnatin Najeriya ta tura buhuwan abinci 1450 ga 'yan gudun hijirarta fiye da dubu 80 wadanda suke kasar Kamaru, makwabciyarta, in ji wani jami'in gwamnatin Najeriya a ranar Lahadi.

Muhammad Sani Sidi, darekta janar hukumar kula da matsalolin gaggawa ta kasa (NEMA), ya bayyana cewa kayayyakin agajin an tura su zuwa ga 'yan gudun hijira da suka bar kasar bayan hare-haren a jahohin dake arewa maso gabashin kasar.

Ya bayyana cewa wadannan kayayyakin an samar da su ne musamman ma domin kai dauki ga 'yan gudun hijiran Najeriya, tare nuna cewa Najeriya za ta ci gaba da tabbatar da kula da hadin kai tare da Kamaru domin tabbatar da cewa dukkan 'yan gudun hijira na zaman rayuwa cikin yanayi mai kyau.

Darekta-janar ya tabbatarwa 'yan gudun hijira cewa gwamnatin Najeriya ba ta manta da su ba kuma za ta yi iyakacin kokarin kwashe zuwa jahohinsu na asili. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China