in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ya kalubalanci bangarorin Mali da rungumi yarjejeniyar sulhu
2016-11-04 11:07:31 cri
Kwamitin sulhun MDD ya fidda wata sanarwa a ranar Alhamis, inda ya yi Allah wadai da yadda a kwanakin baya wasu kungiyoyi masu dauke da makamai suka rika keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta a arewacin kasar, yana mai kalubalantar bangarorin kasar ta Mali, da su aiwatar da yarjejeniyar sulhu da suka sanyawa hannu tun a shekarar bara.

Ban da haka kuma, kwamitin sulhun ya nuna damuwarsa game da yadda ake samun karuwar ayyukan ta'addanci, da aikata laifuka a wurare daban daban na kasar Mali, musamman ma a tsakiya da kudancin kasar, gami da yadda rikici ke kara tsananta tsakanin al'ummomin dake tsakiyar kasar.

A cewar kwamitin sulhun, akwai babban nauyi na tabbatar da kwanciyar hankali da tsaro a wuyan gwamnatin kasar.

Haka zalika, kwamitin sulhun na ganin cewa, har yanzu tawagar wanzar da zaman lafiya dake aiki a kasar Mali ko (MINUSMA), ba ta da cikakken karfi na aiwatar da ayyukanta yadda ya kamata, don haka a cikin sanarwar, kwamitin ya bukaci babban magatakardan MDD da ya dauki matakin da ya wajaba cikin sauri.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China