in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ya yi Allah wadai da harin da aka kai wa sojojin kiyaye zaman lafiya dake kasar Mali
2016-10-05 16:35:45 cri
Kwamitin sulhun MDD ya fidda wata sanarwa a jiya Talata, wadda ke Allah wadai da hare-haren da aka kaiwa tawagar MDD ta jami'an wanzar da zaman lafiya a kasar Mali wato MINUSMA.

Sanarwar ta bayyana cewa, harin da aka kaiwa tawagar MINUSMA a ranar 3 ga watan nan, ta haddasa kisan jami'an kiyaye zaman lafiyar 'yan asalin kasar Chadi su biyu.

Mambobin kwamitin sulhun MDDr sun jajantawa iyalan mutanen da suka mutu, da gwamnatin kasar Chadi, da tawagar MINUSMA, tare da jinjinawa jami'an kiyaye zaman lafiyar da suke gudanar da ayyuka a kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China