Somaliland ba ya halartar zabukan dake gudana a Somaliya ba
Yankin Somaliland na kasar Somaliya, dake neman 'yancinsa, ya bayyana a ranar Lahadi cewa ba ya cikin zabukan dake gudana a yanzu haka a kasar ta Somaliya. Ministan sadarwar Somaliland, Osman Abdullahi Sahardid, ya bayyana cewa yankin Somaliland bai amince da wadanda suke shiga zabukan 'yan majalisu ba dake gudana a Somaliya da sunan yankin ba, inda ya kara da cewa wadannan mutane sun ci amanar yankin Somaliland wajen neman 'yancinsa. (Maman Ada)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku