in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana ci gaba da kai dauki don kashe gobara da ta tashi a dutsen Isra'ila
2016-11-26 13:14:27 cri
An shiga rana ta hudu na samun gobara a yankin dutsen kasar Isra'ila, a ranar 25 ga wannan watan ne, wuta mai tsanani ta tashe a wasu garuruka dake kusa da dutsen birnin Jerusalem.

Bayan kasashen Turkiya, Rasha, Greece, Italiya, Croatia da Cyprus suka tura jiragen saman kashe gobara a yankin, a ranar 25 ga wata kasar Masar da kasar Jordan suka ba da taimako don kashe gobarar ga kasar Isra'ila. Kasar Falasdinu ma ta aike da 'yan kwana kwana da motocin kashe gobara zuwa yankin, haka zalika, jiragen saman kashe gobara masu samfurin Boeing 747 da 'yan kwana kwana da kasar Amurka ta tura sun isa kasar Isra'ila a daren jiya Jumma'a.

A jiya Jumma'a kuma, firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa, dalilin guda daya da ya haddasa tashin gobara a yankin duwatsu shi ne laifin mutane, ya kuma yi gargadi cewa, kasar Isra'ila za ta gurfanar da wadanda suka aikata laifin tashin gobarar a gaban kuliya, kuma bisa labarin da 'yan sandan kasar suka bayar, an ce, tuni an kama mutane 15 wadanda ake zarginsu da hannu a tashin gobarar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China