in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan sandan Isra'ila sun kashe wani Bapalasdine a kusa da birnin Kudus
2015-10-09 09:49:06 cri
A jiya da yamma ne 'yan sanda Isra'ila suka harbe wani Bapalasdine har lahira a yayin wata arangama da ta barke a sansanin 'yan gudun hijirar Shu'fat da ke kusa da birnin Kudus.

Darektan cibiyar lafiya ta al'ummar palasdinawa da ke Ramallah Ahmed Bitawi ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua na kasar Sin cewa,matashin mai suna Wisam Farraj dan shekaru 20 da haihuwa ya mutu ne sakamakon harbin da 'yan sandan Isra'ila suka yi masa a kirji.

Rahotanni na cewa, an kwashe kusan mako guda ana tashin hankali a yammacin gabar kogin Jordan da gabashin birnin Kudus, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar Palasdinawa 7 da Yahudawan Isra'ila 4.

Majiyoyin asibiti na Palasdinawa sun bayyana cewa, daruruwan Palasdinawa ne suka yi taho mu gama da jami'an tsaro, inda suka ke jifan su da duwatsu da bama-baban wuta inda 'yan sanda 9 suka jikkata, baya ga wasu magidanta da dama da suma suka jikkata sanadiyar arangamar.

Bugu da kari, hukumar Palasdinawa ta yi allah-wadai da harin da Yahudawan Isra'ila su ka kaiwa ministanta na sadarwa Allam Musa a kan hanyarsa ta zuwa birnin Nablus da ke kusa da gabar yammacin kogin Jordan

Har yanzu dai gwamnatin Isra'ila ba ta ce komai ba game da wannan lamari.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China