Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya jaddada a yau Jumma'a a nan Beijing cewa, bisa ka'idar kyautata danzon zumuncin da ke tsakanin kasashen Sin da Philippines, kasar Sin ta yarda masuntan Philippines su kama kifi a tekun da ke dab da tsibirin Huangyan, amma hakan bai canja manaufar kasar Sin game da 'yancin mallaka da sanya ido kan tsibirin ba. (Tasallah Yuan)