in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ba za ta ci zarafin kowa ba, amma ba za ta yarda da a yi mata sharri ba
2016-05-09 19:31:13 cri

A yau Litinin ne Lu Kang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya musunta kalaman da ke cewar, wai saboda babban bambancin karfi da ke tsakanin kasashen Sin da Philippines ne ya tilastawa Philippines ta gabatar da kara a gaban kotu dangane da tekun kudancin kasar Sin. Lu ya yi nuni da cewa, wadannan kalamai an yi su ne kawai domin a shafa wa kasar Sin kashin kaji.

Lu Kang ya fadi haka ne a yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing, inda ya kara da cewa, kasar Sin ba za ta ci zarafin kowace kasa ba, amma ba za ta yarda wasu su yi mata sharri ta hanyar da ba ta dace ba. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China