Wakilin shugaban kasar Sin zai halarci bikin bude layin dogo na Habasha zuwa Djibouti
Wakilin shugaban kasar Sin Xi Jinping, kuma shugaban hukumar samar da ci gaba da gudanar da sauye sauye Xu Shaoshi, zai halarci bikin kaddamar da layin dogo, wanda zai hade birnin Addis Ababa na kasar Habasha, da kasar Djibouti, bikin da zai gudana a ranar 5 ga watan Oktoba.
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ne ya bayyana hakan a Juma'ar nan, inda ya ce gwamnatin kasar Habasha ce ta mika sakon gayyatar halartar bikin ga kasar Sin.(Saminu Alhassan)