in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci a mayar da hankali game da hakkoki mutanen dake karkashin ikon IS a Iraqi
2016-11-12 12:52:25 cri
Babban jami'in ofishin kula da hakkin bil adama na MDD Zeid Ra'ad Al Hussein, ya bukaci a gaggauta daukar matakai game da hakkoki da 'yancin fararen hula a birnin Mosul da kuma sauran yankunan dake karkashin ikon kungiyar IS mai da'awar kafa daular musulunci a Iraqi, da suka hada da nema musu hakkokinsu ta fuskar shari'a da kuma samar da maslaha game da makomar rayuwarsu.

Babban jami'in ya tabo wasu batutuwa cikin wani rahoto dake nuna cewa, a yan kwanakin da suka gabata, kungiyar IS ta cigaba da hallaka mutane bisa hukunce hukuncen wasu kotuna da ta kafa na kashin kanta.

Rahotannin sun ce, a ranar Talata data gabata, ISIL ta harbe wasu fafaren hula su 40 a birnin Mosul, bayan da ta zargesu da hada kai da jam'an tsaron kasar Iraqi.

An ce, an ga gawawwakin mutanen ne sanye da tufafi mai launin rawaya, kuma an yi rubutu da launin ja a jikin tufafin dake cewa 'yan leken asirin jami'an tsaron Iraqi, kuma an samu gawawwakin nasu rataye a jikin fala falan wutar lantarki a yankuna da dama na birnin Mosul.

Bugu da kari, da yammacin wannan rana, an harbe wani matashi dan shekaru 27 a yankin Bab al-Jideed dake makwabtaka da tsakiyar birnin Mosul, bayan wani hukuncin da kotun ta ISIL ta yanke masa saboda laifin yin amfani da wayar hannu a Mosul.

Haka zalika, an sake yanke hukuncin rataya kan wasu fararen hula su 6 a ranar 20 ga watan Oktoba a Mosul, bayan an same su da laifin boye layukan wayar hannu, bayan umarnin da ISIL ta bayar na cewa kowane mutum ya mika mata layin wayarsa.(Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China