in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar IS ta ci zarafin jama'ar kasar Iraqi
2015-07-14 11:13:30 cri
Ofishin kula da kare hakkin dan Adam na M.D.D. ya ba da wani rahoto a jiya Litinin, inda ya bayyana cewa, rikicin da aka yi a kasar Iraqi ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama, kuma daga watan Janairu na bara zuwa watan Afrilu na bana, an kashe mutane a kalla dubu 15, tare da jikkatar wasu kimanin dubu 30, musamman ma a yankunan da kungiyar IS ta mamaye, inda aka ci zarafin jama'a har ma aka kashe su.

Rahoton ya ce, kungiyar IS ta kan yi garkuwa ko kisan gilla ga wadanda suke adawa da kungiyar, ko jami'an gwamnatin Iraqi, da sojoji, 'yan jaridu da likitoci, kana kungiyar IS ta kan kashe wadanda ke adawa da akidunsu. Rahoton ya ce, har zuwa yanzu, ana tsare da jama'a kimanin dubu 3.5 mabiya darikar Yazidi, tare da muzguna musu.

A lardunan Anbar da Ninewa, an sanya yara aiki soji. Rahoton ya ce, an kai wasu daga cikinsu zuwa sansanin horaswa dake kasar Siriya, don koya musu amfani da makamai, da yaki da fursunoni.

M.D.D. ta ce, wadannan aika-aikar sun keta dokokin kasa da kasa, kuma wasu daga cikinsu laifuffukan yaki ne da kisan kiyashi.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China