Kungiyar AU ta jaddada damuwarta game da rikicin Libiya
Kwamitin manyan jami'ai na kungiyar tarayyar Afrika (AU) kan Libiya ya sake jaddada a ranar Laraba damuwarsa kan matsalar jin kai da ta tsaro, da kuma makomar siyasa dake cikin rashin tabbas a kasar Libiya. Kwamitin da ya shirya wani zaman taro a ranar Talata a bangaren shugabannin kasashe a Addis Abeba, babban birnin kasar Habasha, ya jaddada goyon bayan kungiyar tarayyar Afrika AU ga tsarin mulkin wucin gadi, dake mayar da hankali da kan wata mafitar siyasa, tare da bayyana cewa yin amfani da karfin damtse ba ita ce hanyar warware rikicin Libiya na yanzu ba. (Maman Ada)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku