in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a martaba dokokin kasa da kasa a yayin da ake daukar matakan soja a Libya, in ji Algeria
2016-02-22 10:09:59 cri
Ministan harkokin wajen kasar Algeriya Ramtane Lamamra ya bayyana a jiya Lahadi cewa, ya kamata a martaba dokokin kasa da kasa yadda ya kamata a yayin da ake daukar matakan soja domin yaki da ta'addanci a kasar Libya.

Mr. Lamamra ya shaidawa kafofin watsa labarai bayan ganawarsa da mataimakin sakataren harkokin wajen kasar Amurka Thomas Shannon cewa, ya kamata a gudanar da matakan soja na yaki da ta'addanci a kasar Libya bisa tsarin dokar kasa da kasa, a sa'i daya kuma, a girmama 'yanci da kuma zaman karko na kasar Libya. Kaza lika, ya ce, kasashen Algeriya da Amurka suna goyon bayan ganin an warware matsalar Libya ta hanyar siyasa.

A nasa bangare kuma, mataimakin sakataren harkokin wajen kasar Amurka Thomas Shannon ya ce, shi da Lamamra sun tattauna kan yadda za a warware matsalar Libya, yaki da ta'addanci da kuma taimaka wa kasar Libya wajen kafa gwamnatin hadaka da za ta kunshi dukkan al'ummomin kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China