in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Afrika da dama za su halarci wani taro a Niamay a karshen watan Oktoba domin tattauna rikicin Libiya
2016-10-04 11:55:23 cri
Wani taro da zai samu halartar wasu shugabannin kasashen Afrika guda goma zai gudana a karshen watan Oktoba a Niamey, babban birnin kasar Nijar, domin tattauna rikicin kasar Libiya, in ji ministan Aljeriya dake kula da harkokin yankin Magreb, kungiyar tarayyar Afrika (AU) da kuma kungiyar kasashen Larabawa, Abdelkader Messahel a ranar Litinin a birnin Algiers.

Wannan taro, bisa kiran kungiyar AU, zai hada kwamitin kasashe biyar wato Mauritaniya, Mali, Burkina Faso, Chadi da Nijar, da kuma kasashen dake makwabtaka da Libiya wadanda suka hada da Tunisiya, Aljeriya, Masar, Sudan, Chadi da Nijar, na cikin tsarin sanya ido kan ricikin Libiya, in ji babban jami'in Aljeriya din a yayin wani taron manema labarai na hadin gwiwa tare da ministan harkokin wajen Libiya, Mohamed Tahar Siyala dake rakiyar shugaban kwamitin mulki na gwamnatin hadaka na kasar Libiya, Faiz Serradj dake ziyarar aiki ta kwanaki biyu a yanzu haka a kasar Aljeriya.

Baya ga taron da aka tsaida shiryawa a Niamey, mista Messahel ya sanar da cewa shugabannin kwamitin kasashe biyar zasu gudanar a karshen watan Oktoba, da wani taron da ya shafi sanya ido kan matsalar Libiya, sai dai ba a ba da wani karin haske ba kan inda za a yi wannan taron.

A nasa bangare, shugaban diflomasiyyar Libiya ya nuna yabo kan rawar da Aljeriya take takawa game da kokarin warware rikicin Libiya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China