in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya yi murnar fara aiki da yarjejeniyar Paris
2016-11-04 19:03:53 cri

A yau Jumma'a ne, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya aika wa Ban Ki-moon, babban magatakardan MDD wasikar murna dangane da yadda yarjejeniyar sauyin yanayi ta Paris ta fara aiki a hukumance.

A cikin wasikarsa, shugaba Xi ya ce, yarjejeniyar Paris ta bude wani sabon babi kan yadda za a magance sauyin yanayi cikin hadin gwiwar kasa da kasa. Kasar Sin tana cike da imanin cewa, nan ba da dadewa ba aikin tinkarar sauyin yanayi zai yi nasara, kasar Sin tana son inganta cudanya da hadin gwiwa da sassa daban daban, ta yadda za ta ba da gudummawa a kokarin da kasashen duniya ke yi na bullo da tsarin daidaita sauyin yanayi bisa adalci. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China