Yau Talata 1 ga wata a nan Beijing, Xi Jinping, babban sakataren Jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya gana da tawagar Jam'iyyar Kuomintang da ke ziyara a nan babban yankin kasar, wadda ke karkashin jagorancin madam Hung Hsiu-chu, shugabar jam'iyyar.
A yayin ganawar, Xi Jinping ya ce, muddin jam'iyyun 2 sun mayar da farfado al'ummar Sinawa tamkar burinsu, sun hada kai al'ummar babban yankin kasar da ma yankin Taiwan tare, sai tabbas ne za a iya kiyaye ci gaban huldar da ke tsakaninsu da kuma bunkasuwa da zaman lafiya a mashigin tekun Taiwan, ta yadda za a iya samun kyakkyawan makoma wajen farfado da al'ummar Sinawa baki daya. (Tasallah Yuan)