in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ziyarar shugaba Xi a kasashen kudu maso gabashin Asiya ta haifar da ci gaban hadin kai da cimma moriyar juna
2016-10-18 09:38:22 cri

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ce ziyarar da shugaba Xi Jinping na lasar Sin ya gudanar a kasashen kudu maso gabashin Asiya, wato Cambodia da Bangladesh, tare da taro na 8 na kungiyar BRICS a kasar India, ya haifar da ci gaban hadin gwiwa, da fadada cimma moriyar juna tsakanin kasashen.

Ya ce yayin taron kungiyar BRICS da ya gudana a birnin Goa na kasar Indiya, shugaba Xi ya gabatar da wasu kudurori 5 wadanda ka iya tallafawa kungiyar, musamman ma a yanayi na matsin tattalin arziki.

Cikin jawabin da ya gabatar, shugaban na Sin ya ce ya dace a bude kofa ga juna, a kuma fidda managartan tsare tsaren ci gaban hadin gwiwa, a kuma fuskanci kalubalen da suka fi fuskantar duniya a yanzu. Sauran kudurorin sun hada da aiwatar manufofi bisa gaskiya da adalci tsakanin kasashen duniya, tare da inganta hadin kai tsakanin hukumomin kasa da kasa.

Ministan harkokin wajen na Sin ya kara da cewa, wannan ziyara ta shugaba Xi, ta tabbatar da manufar kasar Sin a fannin karfafa kawance na diflomasiyya, mai kunshe da gaskiya da adalci, da mutunta juna tsakanin kasashen makwabta, ta hanyar karfafa dangantakar da ke ci gaba da wanzuwa. Har wa yau, za ta dada daidaita tsarin aiwatar da manufar nan ta ziri daya da hanya daya, ta yadda za ta dace da manufofin ci gaban kasashen dake ciki, tare da fadada hadin kai tsakanin kasuwannin kasashe masu tasowa. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China