in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rediyon Sham FM: Dakaru masu adawa da gwamnatin Syria sun yi amfani da makamai masu guba a Aleppo
2016-10-31 10:45:18 cri
Rediyon Sham FM na kasar Syria ya ba da labara a jiya Lahadi cewa, a wannan rana dakaru masu adawa da gwamnati, sun yi amfani da boma-bomai masu hayaki mai guba, a yayin wani farmaki kan birnin Aleppo wanda ke arewacin kasar, lamarin da ya haifar da rasuwar mutum guda, kana wasu 36 na fama da matsalar numfashi.

Wani labarin na daban wanda kamfanin dillancin labaran Syria ya fitar, ya nuna cewa, dakaru masu adawa da gwamnati sun ci gaba da ruwan boma-bomai kan yankin dake karkashin ikon gwamnatin Aleppo, wanda hakan ya haddasa rasuwar mutane biyu, tare kuma da raunata mutane fiye da goma.

A watan Satumbar bana, sojojin gwamnatin Syria sun samu ci gaba a matakan soja da suke dauka, inda kuma suka yiwa yankunan dake gabashin Allepo kawanya, yanki da yanzu haka ke karkashin ikon 'yan adawar gwamnatin kasar.

Daga ranar 20 zuwa 22 ga wata, sojojin gwamnatin Syria sun tsagaita bude wuta na jin kai tsawon kwanaki 3 a birnin Aleppo. Sai dai bayan hakan rikici ya sake barkewa tsakanin sojojin gwamnati da dakarun 'yan adawar.

Kaza lika a ranar 28 ga watan nan, dakaru masu adawar sun kai babban farmaki kan yankunan dake gabashin Aleppo, wadanda ke mallakar gwamnatin wurin, da nufin tarwatsa gungun sojojin gwamnatin wurin da suka yi musu kawanya. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China