Da yake karin haske game da aukuwar lamarin, ministan ma'aikatar watsa labarai a jihar ta kudu maso yamma Ugaas Hassan, ya shaidawa mane ma labarai cewa dakarun kungiyar ta Al-Shabaab sun yiwa wani sansanin sojojin kasar kwantan bauna ne, kafin sojojin su maida martani, lamarin da ya haifar da musayar wuta da kuma rasa rayuka.
Sai dai a hannu guda, ministan ya musanta ikirarin da kungiyar ta Al-Shabaab ta yi, cewa ta kwace wani yankin dake kudu maso yammacin kasar.(Saminu Alhassan)