in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta ba da tallafin dalar Amurka miliyan 2 ga shirin WFP don tallafawa Somaliya
2016-10-19 09:33:06 cri
Gwamnatin kasar Sin ta ba da tallafin kudi kimanin dalar Amurka miliyan 2 ga shirin samar da abinci na MDD, WFP, domin amfani da su wajen samar da kayayyakin tallafi ga kasar Somaliya, wacce ke fama da matsalar kamfar abinci sakamakon mummunan fari da kasar ke fama da shi.

An gudanar da bikin mika tallafin ne a Mogadishu, babban birnin kasar Somaliya, WFP ta yabawa gwamnatin Sin bisa wannan namijin kokari.

Daraktan shirin WFP dake Somali Laurent Bukera, ya ce za'a yi amfani da kudaden tallafin da kasar Sin ta bayar wajen samar da abinci mai gina jiki ga yara kanana, da mata wadanda ke fama da matsalar karancin abinci mai gina jiki.

Jakadan kasar Sin a Somaliya, Wei Hongtian, ya fada a lokacin bikin cewa, "kasar Sin tana ci gaba kuma za ta ci gaba da kasancewa babbar aminiya kuma mai taimakawa gwamnatin Somaliya da hukumomin MDD, ciki har da shirin hukumar WFP.

Ministan cikin gidan Somaliya Abdurashid Muhamed Hidig, ya yabawa gwamnatin kasar Sin a madadain gwamnatin kasar Somaliya, ya kara da cewa gwamnatin kasar Sin da alummar Sinawa sun jima suna bada taimako wajen cigaban kasar Somaliya. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China