Mahalarta taron dai sun maida hankali ga nazarin dabarun hadin gwiwa tsakanin sassan masu ruwa da tsaki a ayyukan tawagar ta AMISOM. Sassan sun kunshi bangaren sojoji da fararen hula, tare da jami'an wanzar da zaman lafiya masu tallafawa samar da agajin jin kai.
Kaza lika an tattauna game da tsare tsaren da aka tanada, don gane da ayyukan hadin gwiwa tsakanin AMISOM da sauran hukumomin dake aikin jin kai a kasar.
Masana na ganin ya zama wajibi a kara kwazo wajen tattaunawa, da nufin tunkarar kalubalolin dake fuskantar ayyukan AMISOM, dama na sauran masu bada agaji dake aiki a Somaliya.(Saminu Alhassan)