Kakakin hukumar tsaron cikin gidan kasar Abdikamil Moalim Shukri, shi ne ya tabbatar da hakan a Talatar nan, yana mai cewa maharan sun harbe Abdiaziz Araye ne da bindiga jiya da almuru, sa'an nan kuma suka tsere.
Kafin rasuwar sa Mr. Araye, jami'in tsaron farin kaya ne dake aiki a gundumar Waberi.
Yanzu haka dai jami'an tsaro na ci gaba da farautar wadannan 'yan bindiga.(Saminu Alhassan)