Omar Muhammad Abdulle, shi ne shugaban hukumar zartaswa ta tarayya na hukumar zaben kasar, ya fada cikin wata sanarwa cewa, za'a kammala zaben karamar majalisar ne zuwa ranar 10 ga watan Nuwamba.
Bayan an kammala zaben majalaisun dokokin biyu, sabbin 'yan majalisun da aka zabe ne za su zabi shugaban kasar a ranar 30 ga watan Nuwamba.
Ya kara da cewa, ana sa ran za'a cimma kudirin baiwa mata kaso 30 cikin 100 na kujerun majalisar dokokin kasar. (Ahmad Fagam)