in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Yemen ya ki amincewa da shirin zaman lafiya na MDD
2016-10-30 13:38:54 cri
Jiya Asabar 29 ga wata, shugaban kasar Yemen Abdu Rabbin Mansour Hady ya nuna kin amincewa da shirin zaman lafiya da manzom musamman na MDD dake kula da harkokin kasar Yemen Ismail Ould Cheikh Ahmed ya gabatar, wanda ake sa ran shirin zai iya kawon karshen rikicin da ake fama da shi a kasar Yemen a halin yanzu.

Bisa labaran da aka samu, an ce, shugaba Hady ya bayyana kiyayyarsa kan wannan shiri bisa dukkan fannoni a yayin wata ganawa tare da Mr. Ahmed a birnin Riyadh na kasar Saudiya a ranar Asabar.

Haka kuma, wani shafin intanet na kasar Yemen ya ruwaito maganar shugaba Hady cewa, shirin zaman lafiya da MDD ta gabatar ba zai samar wa kasar Yemen zaman lafiya ba, illa kawai zai bude wata kofa ta daban ga al'ummomin kasar shiga cikin karin barazana da rikice-rikice.

A halin yanzu, ba a yi bayani kan shirin zaman lafiya da Mr. Ahmed ya gabatar ba, amma wasu kafofin watsa labarai sun bayyana cewa, ana fatan kafa wata gwamnatin hadin gwiwa a tsakanin gwamnatin kasar da jam'iyyar adawa cikin wannan shiri. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China