in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman na MDD ya shelanta kawo karshen shawarwarin sulhu kan batun Yemen a Kuwait
2016-08-07 14:08:44 cri
A jiya Asabar, manzon musamman na MDD kan batun Yemen, Ismail Ould Cheikh Ahmed ya shelanta cewa, an kawo karshen shawarwarin sulhu kan batun Yemen a Kuwait, sai dai bangarori masu aramgama da juna ba su samu cigaba na a zo a gani ba.

Duk da haka, a gun taron manema labaru da aka shirya, Ismail Ould Cheikh Ahmed ya sanar da cewa, za a farfado da shawarwarin tsakanin gwamnatin Yemen da kungiyar Houthis nan da wata guda.

Gwamnatin Yemen ta shelanta amincewa da daddale daftarin yarjejeniyar da MDD ta bayar ga bangarorin biyu a ranar 31 ga watan Yuli, da fatan hakan zai sa kaimi ga tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar. Amma kungiyar Houthis ta ki amincewa da wannan daftarin yajejeniyar, kuma ta bukaci a kafa hadaddiyar gwamnatin hadin kan kasar ta yadda za ta samu wakilci cikinta.

A ranar 28 ga watan Yuli, kungiyar Houthis da tsohon shugaban kasar Ali Saleh suka sanar da kafa kwamitin shugaban kasa domin kulawa da harkokin kasar. Kana a jiya ne aka nada membobin kwamitin, tare da shelanta cewa, za a kafa gwamnatin kasar a nan gaba.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China