in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bangarori dake musayar wuta a Yemen sun yi musayar fursunoni 224 a tsakaninsu a kwanaki biyu da suka wuce
2016-06-20 12:16:35 cri
A jiya Lahadi, gwamnatin kasar Yemen da kungiyar Houthis mai dauke da makamai sun ba da wata sanarwa, inda suka tabbatar da batun canza fursunonin yaki 224 a tsakaninsu cikin kwanaki biyu da suka wuce.

A jiya, sojojin Yemen da dakarun Houthis, kowanensu sun saki fursunonin yaki 15 a lardin Al Jawf dake arewa maso gabashin kasar. Hukumomin yada labarai na bangarorin biyu sun ba da sanarwa domin tabbatar da wannan batu.

A ranar Asabar 18 ga wata, bangarorin biyu sun canza fursunonin yaki 194 a lardin Taiz, ciki har da fursunonin yaki daga kungiyar Houthis 118 da fursunonin yaki daga sojojin Yemen 76.

Musayar fursunonin yakin ya zama wani bangare na yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta Yemen dake karkashin jagorancin MDD. Bangarorin sun rabbata hannu kan yarjejeniyar a watan Afrilun bana, da fatan za a kawo karshen wannan yaki. Amma wannan yarjejeniya ba ta fara aiki ba tun daga daddale ta. Bisa shiga tsakani na MDD, yanzu ana yin shawarwari cikin lumana kan batun Yemen a Kuwait.

A watan Satumba na shekarar 2014, kungiyar Houthis ta mamaye birnin Sanaa, hedkwatar kasar Yemen. Shugaban kasar Abdu-Rabbu Mansour Hadi da 'yan majalisar dokokinsa sun yi gudun hijira zuwa Saudiya. A watan Maris na bara, Saudiya da wasu sauran kasashen duniya sun fara daukar matakan soja kan kungiyar Houthis.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China