in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shigar Masar a cikin kwamitin kare hakkin dan adam na MDD na shaida wani halin amincewa
2016-10-30 12:10:39 cri

Shigar Masar a cikin kwamitin kare hakkin dan adam na MDD na shaida wani muhimmin matsayinta da karfafa karbuwarta a cikin gamayyar kasa da kasa, in ji Ahmed Abu Zeid, kakakin ma'aikatar harkokin wajen Masar a cikin wata sanarwa a ranar Asabar.

Zaben a cikin kwamitin kare hakkin dan adam ya kasance wata alama ta cewa, Masar tana taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa tsaro da kwanciyar hankali a Gabas ta Tsakiya da kuma Afrika, har ma da karfafa ka'idojin 'yancin kasa da kasa da girmama kundin tsarin MDD, a cewar wannan sanarwa.

An zabi Masar a ranar Jumma'a bisa wa'adin shekaru uku tun daga ranar 1 ga watan Janairun shekarar 2017. Wannan yana bayyana wata sabuwar nasarar diplomasiyya da tabbatarwa na amincewa kasa da kasa game da wannan kasar Larabawa, in ji kakakin.

Haka kuma ya bayyana farin cikin Masar game da dukkan kasashen da suka nuna mata goyon baya wajen zabenta. A tsawon wannan sabon wa'adi, kasar Masar za ta jajirce wajen kara karfafa karfin kwamitin a cikin aikinsa na bunkasa da kare 'yancin dan adam, in ji mista Abu Zeid. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China