in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Masar ya yi kira da a warware matsalar bakin haure ta hanyar tsara doka
2016-09-25 12:48:40 cri
Shugaban kasar Masar Abdel-Fattah al-Sisi ya bayar da sanarwa a jiya ranar 24 ga wata, inda ya yi kira ga majalisar dokokin kasar da ta yi bincike kan daftarin doka da gwamnatin kasar ta bayar game da batun warware matsalar bakin haure, tare da warware matsalar ta hanyar tsara doka.

Al-Sisi ya bayyana cewa, ya riga ya bada umurnin shugaba, inda ya bukaci gwamnatin kasar da ta hada kai da majalisar dokokin kasar wajen kammala yin bincike kan wannan daftarin doka, da bukatar hukumomin kiyaye tsaro na kasar da su dauki matakan yaki da masu fataucin mutane.

An yi hadarin nutsewar jirgin ruwa dake dauke da masu neman satar shigowa nahiyar Turai a tekun Atlantic na arewacin kasar Masar a ranar 21 ga wannan wata, wanda ya haddasa mutuwar mutane 164 ya zuwa ranar 24 ga wata.

Bayan hadarin, kasar Masar ta kama mutane 6 da aka zarge su da aikata laifin fataucin mutane da jigilar bakin haure. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China