in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Masar sun kai hari ta sama kan sansanonin masu tsattsauran ra'ayi
2016-10-16 13:24:40 cri
A jiya Asabar 15 ga wata, sojojin Masar sun kai hari ta sama kan sansanonin masu tsattsauran ra'ayi dake jihar Sinai ta arewa, domin murkushe dakarun da suka kai hari kan wata tashar bincike ta rundunar soja a ranar Jumma'a 14 ga wata. Rundunar sojan Masar ta ba da labarin cewa, a kalla dai dakaru masu tsattsauran ra'ayi 100 ne suka mutu sakamakon haka, yayin da wasu dakaru 40 suka jikkata.

A ranar Jumma'a 14 ga wata, an kai hari kan wata tashar bincike ta rundunar sojan Masar a jihar Sinai ta arewa, wanda ya haddasa mutuwar sojoji 12, yayin da wasu sojoji 6 suka ji rauni. Kana wasu dakaru 15 suka mutu a cikin musayar wuta.

A daren ranar 14 ga wata, reshen kungiyar IS a jihar Sinai ta arewa ya ba da sanarwa a shafinsa na yanar gizo cewa, inda ta yi shelar daukar alhakin kai wannan hari.

Bayan harin, shugaban Masar Abdul Fatah Al-Sisi ya ba da sanarwar, inda ya mika ta'aziyya ga iyalan wadanda suka mutu, tare da nuna cewa, wannan hari zai karfafa niyyar kasar wajen yaki da ta'addanci.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China