Sin za ta ci gaba da tabbatar da muhimmiyar rawar da MDD ta taka a kan harkokin kasa da kasa
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya bayyana a Talatar nan cewa, shekarar bana shekara ce ta cika shekaru 45 tun bayan da kasar Sin ta sake samun matsayinta a MDD, kuma Sin din za ta ci gaba da tabbatar da oda, da tsarin kasa da kasa bisa kundin tsarin mulkin MDD da ka'idojinta, da nuna goyon baya ga MDD wajen gudanar da ayyukanta.
Duk a ranar Talata kuma, hukumar MDD mai kula da tattalin arziki da zamantakewar al'ummar Asiya da tekun Pasific, mai cibiya a birnin Bangkok na kasar Thailand, ta gudanar da wani biki a yau, na murnar ranar cika shekaru 45 da komawar Sin MDD. (Zainab)