in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afirka ta kudu ta bukaci jama'a da su tofa albarkacin bakinsu game da dokar yaki da manyan laifuffuka
2016-10-25 09:21:15 cri
Gwamnatin Afirka ta kudu ta bukaci 'yan kasar da su tofa albarkacin bakinsu game da dokar yaki da manyan laifuffuka da kalaman nuna kyama da aka bullo da ita a kasar.

Ministan shari'a da gyara halayen 'yan kasa Micheal Masutha ya ce, an dauki wannan mataki ne, sakamakon kalaman nuna wariya da wasu abubuwan nuna kyama da ke faruwa a baya-bayan a kasar, don magance irin abubuwan da suka faru a zamanin nuna wariyar launin fata.

Ministan ya shaidawa taron manema labarai a birnin Pretoria cewa, a makon da ya gabata ne majalisar zartaswar kasar ta amince jama'a su tofa albarkacin bakinsu game da dokar, lamarin da ya haifar da kalaman nuna kyama. Wannan ya sa aka bullo da matakan magance wadannan matsaloli tun kafin abubuwa su dagule. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China