in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Afirka ta kudu ta fara shirin ficewa daga kotun ICC
2016-10-21 20:53:27 cri
Ministan shari'a da gyara halaye na kasar Afirka ta kudu Micheal Masutha ya tabbatar a yau Jumma'a cewa, kasar sa ta fara shirin ficewa daga kotun hukunta manyan lafifuffuka ta duniya ICC.

Ministan ya shaidawa taron manema labarai a birnin Pretoria cewa, tuni kasar ta rubutawa babban sakataren MDD Ban Ki-moon wasika game da hakan, matakin da zai baiwa kasar damar ficewa daga kotun shekara guda bayan babban sakataren MDDr ya samu wannan wasika.

Minista Mashutha ya ce,kasar Afirka ta kudu dai tana fuskantar matsin lamba ne karkashin yarjejeniyar Rome wadda ta kafa kotun ICC, yarjejeniyar da ke tilastawa kasar da ke zama mambar kotun na kama mutanen da ke da dokar kariya, amma kotun ta ke neman kama su.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China