in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyyar ANC ta yi kira ga 'yan kasar Afirka ta kudu da su yi koyi da darusan nan da suka faru a Marikana
2016-08-17 10:01:36 cri
Jam'iyyar ANC mai mulki a kasar Afirka ta kudu, ta yi kira ga daukacin 'yan kasar da su rika amfani da hanyoyin tattaunwa wajen warware duk wata matsala da rashin jituwa da ta kunno kai a wuraren ayyukansu, a matsayin darasi game da abin da ya faru a mahakar Marikana.

Jam'iyyar ta yi wannan kiran ne yayin da kasar ta ke bikin tunawa da masu aikin hakar ma'adinai 34 da 'yan sanda suka harbe shekaru 4 da suka gabata. Al'amari mafi muni da ya faru a bangaren hakar ma'adinan kasar tun bayan zamanin nuna wariyar launin fata.

Kakakin jam'iyyar ANC Zizi Kodwa ya ce, koyi da abubuwan da suka faru, za su taimakawa kasar wajen ganin ba ta sake faduwa cikin irin wannan al'amari ba. Ya ce wajibi ne hukumomi su rika kare 'yancin ma'aikata, ciki har da samar musu da yanayin aiki mai kyau, kuma wannan shi ne musabbin tashin hankalin na Marikana.

A saboda haka, jam'iyyar ta yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki, da su yi amfani da wannan lokaci wajen yin aiki tare, don ganin an dawo da zaman lafiya a wannan yanki.

Mahukuntan kasar Afirka ta kudun dai sun yi alkawarin magance matsalolin da ke addabar bangaren jin dadin jama'a da na tattalin arzikin kasar.

A ranar 16 ga watan Agustan shekarar 2013 wato shekaru 4 da suka gabata ne, aka yi arangama tsakanin masu aikin hakar ma'adinai da 'yan sanda a mahakar Lonmin da ke Marikana a lardin North West.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China