in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta tabbatar da samun sakon Afirka ta kudu dangane da ficewarta daga ICC
2016-10-22 12:52:21 cri
Kakakin babban sakataren MDD Stephane Dujarric, a jiya Jumma'a ya tabbatar da cewa, MDD ta samu sakon da kasar Afirka ta kudu ta mika mata dangane da ficewa daga kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa wato (ICC), kuma Ban Ki-moon ya nuna takaicinsa game da wannan matakin da kasar ta dauka.

A gun taron manema labarai da aka shirya a wannan rana, Stephane Dujarric ya ce, bayan da ya samu wasikar, sashen kula da harkokin shari'a na MDD ya fara aiki a kan batun. Kasar Afirka ta kudu na daya daga cikin kasashen da suka fara rattaba hannu a kan yarjejeniyar Rome ta kafa Kotun hukunta manyan laifuffuka ta kasa da kasa. (Lubabatu Lei)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China