in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da bikin gama karatun koyon Sinanci na ma'aikatan kwastam na kasar Najeriya karo na farko
2016-10-21 10:40:18 cri
A jiya Alhamis ne aka gudanar da bikin kammala karatun koyon Sinanci, na ma'aikatan kwastam a tarayyar Nijeriya karo na farko, kwas din da ya gudana a ofishin kwastam dake filin jiragen saman birnin Abuja fadar mulkin kasar.

Wannan ne karo na farko da ofishin jakadancin Sin dake Najeriya, da hukumar kwastam ta Najeriya suka dauki nauyin gudanar da wannan kwas. Jami'an kwastam na Najeriyar 40 ne suka halarci bikin kammala karatun.

An ce, an raba kwas din gida 7, inda ake gudanar da ko wane kashi cikin watanni 7. Ana koyar da ma'aikatan kwastam din Najeriya kimanin 300 yaren Sinanci. Bayan kammala karatun, za su iya amfani da yaren wajen karbar masu bukatar amfani da Sinanci a filin jiragen saman birnin Abuja. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China