Gwamnatin ta kuma jaddada cewa, ba za ta yi kasa a gwiwa ba, game da shirin ta na yaki da cin hanci da karbar rashawa.(Vanguard)
Majalisar dattawan Najeriya ta bukaci dukkan bangarori a tattaunawar da ta kai ga sakin 'yan matan Chibok 21, da su tabbatar da cewa,an saki ragowar mutanen da ke tsare a hannun mayakan na Boko Haram.
Majalisar dattawan ta kuma godewa wadanda suka shiga tsakani game da sakin 'yan matan sakandaren na Chibok guda 21. Sai dai kuma ta ce, akwai wasu mutane da dama wadanda Boko Haram suke tsare da su da ba a ba da rahotonsu ba. Ta ce kamata ya yi a fadada tattaunawar da ake yi don ganin an saki karin wadanda ake tsare da su, maimakon 'yan matan chibok kadai.(The Punch)