Nijeriya tana shirin gaggauta aiwatar da yarjejeniyar musayar kudinta da kudin Sin RMB
Jaridar Vanguard da ake wallafawa a Nijeriya ta ruwaito gwamnan bankin kasar Godwin Emefiele a taron asusun ba da lamuni na duniya da bankin duniya na lokacin kaka a kwanakin baya, yana cewa, jami'an gwamnatin kasar Nijeriya suna ganawa da bangaren kasar Sin don gaggauta aiwatar da yarjejeniyar musayar kudin kasar da kudin Sin RMB. Mr Godwin ya jaddada cewa, yarjejeniyar za ta sassauta matsin lamba da kasar Nijeriya ke fuskanta a fannin musayar kudaden waje, da rage bukatunta na dalar Amurka. (Zainab)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku