in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Muhimman labarai daga wasu jaridun Najeriya
2016-10-18 21:05:50 cri
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya bayyana kudurin gwamnatinsa na ci gaba da tattaunawa da kungiyar Boko Haram don ganin ta saki ragowar 'yan matan makarantar Chibok da ta ke tsare da su.

Shugaba Buhari ya ce, a shirye ya ke ya ci gaba da tattaunawa da kungiyar muddin za ta amince ta sanya kungiyoyin kasa da kasa kamar kungiyar ba da agaji ta kasa da kasa ta Red Cross(Daily Trust)

Karamin ministan albarkartun man fetur na Najeriya Ibe Kachikwu ya bayyana a yau Litinin cewa, mahukuntan kasar sun fara yin shawarwari da gwamnatin kasar Indiya kan yadda za ta fara biyan dala biliyan 15 na danyen man da ta saya daga kasar.(The Punch)

Majalisar dokokin Najeriya ta yanke shawarar ranto kudade daga bankuna wajen biyan ma'aikatanta kudadensu na albashi da alawus-alawus, sakamakon karancin kudin da ta ke fuskanta. Amma matakin bai shafi kudaden da 'yan majalisar ke bukata wajen tafiyar da harkokin majalisa, albashi, alawus-alawus da na mataimakansu ba.(The Guardian)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China