Rahotanni daga kasar Somaliya na cewa, tawagar kungiyar tarayyar Afirka da ke aikin wanzar da zaman lafiya a kasar Somaliya(AMISON) ta ce dakarunta sun yi nasarar kashe a kalla mayakan kungiyar Al-Shabaab 7 tare da jikkata wasu 11 a yayin da mayakan kungiyar suka yi musu kwanton bauna a garin Janale da ke kudancin Somaliya a yammacin ranar Talata.
Mazauna yankin sun ce kwanson albarusai da dama sun fada a tsakiya da kuma kusa da wajen garin, lamarin da ya haddasa mutuwar 'yan kungiyar ta Al-Shabaab da dama.
Sai dai har yanzu kungiyar wadda ta shafe shekaru da dama tana fada da gwamnatin Somaliya ba ta yi wani karin haske ba.((brahim)