in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AMISOM ta karyata rahotannin kashe fararen hula a Somaliya
2016-10-07 12:16:49 cri
Tawagar kungiyar tarayyar Afirka da ke aikin wanzar da zaman lafiya a kasar Somaliya(AMISOM) ta karyata rahotanni da ke cewa, hare-haren da dakaruntra suka kai a garin Janale da ke kudancin Somaliya yayin fafatawa da mayakan kungiyar Al-Shabaab a ranar Talata ya yi sanadiyar mutuwar fafaren hula 5.

A wata sanarwa da kungiyar ta rabawa manema labarai a jiya Alhamis, AMISOM ta ce, wurin da dakarunta suka halaka mayakan kungiyar Al-Shabaab 7 yana nesa da yankunan da jama'a ke zaune. Haka kuma tawagar tana ba da muhimmanci sosai ga tsaro da kare rayukan fararen hula a duk lokacin da ta ke gudanar da ayyukanta.

Kafofin watsa labarai a yankin suna ikararin cewa, an kashe fararen hula biyar kana wasu da dama kuma suka jikkata a harin da dakarun na AMISOM suka kaddamar a wani yankin da ke kusa da garin Janale da ke Lower Shabelle.

Tawagar AMISOM dai tana taimakawa sojojin Somaliya ne a yakin da suke yi da mayakan Al-Shabaab, wadanda suka sha kaddamar da hare-hare a kasar.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China